Surah Al-Masad ( The Palm Fibre )

Hausa

Surah Al-Masad ( The Palm Fibre ) - Aya count 5

تَبَّتْ يَدَآ أَبِى لَهَبٍۢ وَتَبَّ ﴿١﴾

Hannãye biyu na Abũlahabi sun halaka, kuma ya halaka.

مَآ أَغْنَىٰ عَنْهُ مَالُهُۥ وَمَا كَسَبَ ﴿٢﴾

Dũkiyarsa ba ta tsare masa kõme ba, da abin da ya tãra.

سَيَصْلَىٰ نَارًۭا ذَاتَ لَهَبٍۢ ﴿٣﴾

Zã ya shiga wuta mai hũruwa.

وَٱمْرَأَتُهُۥ حَمَّالَةَ ٱلْحَطَبِ ﴿٤﴾

Tãre da matarsa mai ɗaukar itacen (wuta).

فِى جِيدِهَا حَبْلٌۭ مِّن مَّسَدٍۭ ﴿٥﴾

A cikin kyakkyãwan wuyanta akwai igiya ta kaba (Rãnar ¡iyãma).