Surah Al-Fatihah ( The Opening )

Hausa

Surah Al-Fatihah ( The Opening ) - Aya count 7

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ ﴿١﴾

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

ٱلْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ ﴿٢﴾

Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;

ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ ﴿٣﴾

Mai rahama, Mai jin ƙai;

مَٰلِكِ يَوْمِ ٱلدِّينِ ﴿٤﴾

Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.

إِيَّاكَ نَعْبُدُ وَإِيَّاكَ نَسْتَعِينُ ﴿٥﴾

Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.

ٱهْدِنَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلْمُسْتَقِيمَ ﴿٦﴾

Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.

صِرَٰطَ ٱلَّذِينَ أَنْعَمْتَ عَلَيْهِمْ غَيْرِ ٱلْمَغْضُوبِ عَلَيْهِمْ وَلَا ٱلضَّآلِّينَ ﴿٧﴾

Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.